
Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta na halarta Taron Sauyin Yanayi na Majalisar Ɗinkin Duniya (wato COP27) a garin Sharm el-Sheikh na ƙasar Masar, a ranar Litinin.
A taron, mahalarta daga sassa daban-daban na duniya su na tattauna muhimman batutuwa da su ka danganci sauyawar yanayi.