Yarinya ‘yar shekaru 14 ta kafa tarihi

0
58
Fatima Adamu Maiƙusa

Daga wakilinmu

Daga jahar Gombe yarinya  mai suna Fatima Adamu Maikusa, ta kafa tarihin lambobin yabo na duniya har guda 7 a ilimin lissafi.

Fatima Adamu Maikusa wadda ta kasance ‘yar baiwa daga jahar Gomben Najeriya, ta lashe lambobin yabo

mabambanta guda 7 a faɗin duniya. Wannan ya sa ta kafa tarihin zama ta farko a Najeriya da ta lashe wannan kambu.

Tun Fatima na da shekara 9 ta fara nuna hazaƙa, kuma ta zama madubin dubawa ga sauran yara mata.

A yanzu haka tana matakin na 11 a makarantar Nigerian Turkish International School (NTIS) da ke Kano.

Gasannin da Fatima ta lashe akwai American Mathematics Competition (AMC), International Eduversal Mathematics Competition a Jakarta da Indonesia. Da wasu gasanni a Bangkok, Thailand and Kangouro Sans.

Sannan akwai gasar Future Intelligence Student Olympiad (FIOS), Mathematics Without Borders a Bulgaria sai kuma Komodo Festival a Indonesia.

Leave a Reply